Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Kaddamar da Sabon Shafin Daukar Ma'aikata 10,000

Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Kaddamar da Sabon Shafin Daukar Ma'aikata 10,000

A wani mataki na bunkasa rayuwar al’umma da kuma karfafa ma’aikata, Gwamnatin Jihar Bauchi ta kaddamar da wani sabon shafin yanar gizo na daukar ma’aikata, wanda ke dauke da sama da ayyuka 10,000 a sassa daban-daban na Ma’aikatun Gwamnati, Hukumoji da Sashen Gudanarwa (MDAs).

Wannan shiri na gwamnati karkashin jagorancin mai girma Gwamna, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, na da nufin samar da damammaki ga matasa da masu kwarewa domin su samu damar bada gudummawa a ci gaban jiharsu. An tabbatar da cewa tsarin daukar aikin zai kasance cikin sauki, da sauri, kuma a bude ba tare da son zuciya ba, domin tabbatar da adalci ga kowane dan takara.

Dama Ga Kowa da Kowa

Shafin daukar aikin na gwamnati, wanda ake samu a recruitment.bauchistate.gov.ng, ya bude ga dukkan ‘yan jihar da ke sha’awar neman aiki. Ana bukatar masu sha’awa su ziyarci shafin, su duba guraben ayyukan da ake da su, sannan su cika fam din neman aikin cikin hanzari. An tsara shafin ne ta yadda kowa zai iya amfani da shi cikin sauki tare da cikakken bayani da umarni.

Wannan daukar aiki ya shafi fannoni da dama ciki har da ilimi, kiwon lafiya, gine-gine, shugabanci da sauransu. Gwamnatin jihar ta kuduri aniyar gina sahihin rundunar ma’aikata masu basira da kwarewa, domin gina makoma mai kyau ga daukacin jama’ar jihar.

Ranar Karshe na Cikawa

Za a karbi aikace-aikacen har zuwa ranar 26 ga Mayu, 2025. Don haka ana kira ga ‘yan jihar Bauchi da su gaggauta cikawa tun kafin wa’adin ya kare. Gwamnati ta ja kunnen cewa aikace-aikacen da suka zo bayan lokacin da aka kayyade ba za su samu la’akari ba.

Domin karin bayani, ziyarci: recruitment.bauchistate.gov.ng ko tuntubi ofishin yada labarai na Gwamnatin Jihar Bauchi.